Za a Binciki Netanyahu Kan Zargin Zubewar Sirrin Ofis: Rahotanni

 


Babban lauyan Isra’ila, Gali Baharav-Miara, ya ba wa hukumomi izinin binciken ofishin Firayim Minista Benjamin Netanyahu dangane da zargin zubewar wasu takardun sirri.


Kafofin yada labaran Isra’ila sun ruwaito a ranar Juma’a cewa izinin da Baharav-Miara ya bayar yana nufin cewa hukumomin da ke gudanar da bincike za su iya bincikar Netanyahu kansa.


A ranar Lahadi, hukumar tsaron Isra'ila (Shin Bet) ta sanar da cafke wasu mutane da dama, ciki har da wani mai magana da yawun Netanyahu, bisa zargin su da zubewar bayanan sirri dangane da yakin kisan kare dangi da ake kaiwa a Zirin Gaza.


Wani alkalin Isra’ila ya bayyana cewa zubewar wannan bayanan sirri na iya haifar da “babban illa” ga kokarin ‘yantar da wasu fursunonin Isra’ila da Hamas ke tsare da su a Gaza.


Netanyahu ya musanta cewa ofishinsa yana da hannu a lamarin, yana mai bayyana a cikin wata sanarwa cewa ba a binciki ko kuma kama kowa daga ofishinsa ba.


A gefe guda kuma, rahotanni a ranar Alhamis sun ce ofishin Netanyahu ya tattara wasu bayanan bidiyo masu muhimmanci na tsaron tsohon Ministan Harkokin Tsaro Yoav Gallant da wani jami'in soja da ya yi aiki a ofishin firayim ministan.


Rahotannin sun bayyana cewa lamarin yana da alaka da wasu zarge-zargen da suka kunno kai kan ofishin Netanyahu a kwanakin baya.


Ofishin firayim ministan Isra’ila ya sake musanta wadannan rahotanni na zubewar bayanai, yana mai kira su da “batanci.”


Wannan lamarin na faruwa ne a yayin da gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da mummunan yakin da ta ke kaiwa a Gaza wanda aka fara a ranar 7 ga watan Oktoban bara, wanda ya yi sanadin mutuwar fiye da Falasdinawa 43,500.

Post a Comment

Previous Post Next Post