Gwamnatin Isra’ila ta sanar cewa sojojinta ba za su janye daga Labanon ba zuwa ranar Lahadi, 26 ga Janairu, wanda ya saba wa yarjejeniyar tsagaita wuta da ta kawo karshen watannin hare-hare kan ƙasar Larabawan.
Matakin jinkirin janyewar ya zo ne bayan makonni na maganganu da ke nuna cewa Isra’ila ta shirya ci gaba da zama a akalla wurare biyar a kudancin Labanon.
Da yake tabbatar da cewa Isra’ila ba za ta cika wa’adin ranar 26 ga Janairu ba, ofishin Firayim Minista Benjamin Netanyahu ya zargi Beirut da rashin cikakken aiwatar da yarjejeniyar.
A cikin wata sanarwa ranar Juma’a, ofishin ya ce: “Tsarin janye sojoji yana da sharadin cewa sojojin Labanon su mamaye kudancin Labanon tare da tabbatar da cikakken aiwatar da yarjejeniyar, sannan Hezbollah ta janye zuwa bayan Kogin Litani.”
Sanarwar ta ce Isra’ila ta ɗauki tsagaita wutar a matsayin “ba a aiwatar da ita gaba ɗaya ba” kuma cewa “tsarin janyewa sannu a hankali zai ci gaba tare da cikakken haɗin gwiwa da Amurka.”
A ƙarƙashin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka rattaba hannu a watan Nuwamba, sojojin Isra’ila za su janye daga Labanon yayin da sojojin Labanon za su mamaye kudancin ƙasar cikin kwanaki 60, waɗanda zaya kare ranar 26 ga Janairu.
Kungiyar Hezbollah ta yi kira ga gwamnatin Labanon da sauran bangarori su tabbatar da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra’ila.
Kungiyar ta bayyana cewa duk wata hujja da za ta hana cikakken aiwatar da yarjejeniyar ba za ta yarda da ita ba.
Hezbollah ta ce duk wani yiwuwar jinkiri daga Isra’ila wajen janye sojojinta daga kudancin Labanon zai zama take hurumin mulkin ƙasar Larabawan.
Kungiyar ta bayar da wannan gargaɗi a wata sanarwa ranar Alhamis bayan kafofin watsa labarai na Isra’ila sun bayyana cewa gwamnatin ƙasar ta nemi Amurka ta ba ta ƙarin kwanaki 30, fiye da kwanaki 60 da aka tanada a yarjejeniyar tsagaita wuta da Hezbollah.
A wannan makon, wani ɗan majalisar dokoki na Hezbollah ya bayyana cewa gazawar cika wa’adin da aka kayyade zai sa yarjejeniyar tsagaita wuta ta rushe.
“Muna cikin jiran ranar 26 ga Janairu, ranar da yarjejeniyar tsagaita wuta ta tanadi cikakken janyewar Isra’ila daga ƙasar Labanon,” in ji Ali Fayyad. “Idan abokan gaba na Isra’ila ba su cika wannan ba, hakan na nufin rushewar yarjejeniyar tsagaita wuta.”
Shugaban Hezbollah Sheikh Naim Qassem ya ce Isra’ila ta aikata ɗaruruwan karya yarjejeniyar tsagaita wuta.
“Muna da haƙuri da waɗannan take-taken don ba wa gwamnatin Labanon, wadda ke da alhakin yarjejeniyar, tare da masu tallafawa na duniya, damar aiwatar da ita. Amma ina kira gare ku kada ku gwada haƙurinmu,” in ji shi a makon da ya gabata.
Isra’ila ta tilastawa kanta amincewa da yarjejeniyar tsagaita wuta da Hezbollah a ranar 27 ga Nuwamba, 2024, bayan ta sha babban rashi a filin daga kuma ta kasa cimma burinta duk da kashe sama da mutane 4,000 a Labanon.
Kafofin watsa labarai na Channel 13 na Isra’ila sun ruwaito cewa Firayim Minista Benjamin Netanyahu ya nemi gwamnatin Shugaban Amurka Donald Trump ta ba Isra’ila damar ci gaba da mamaye wuraren soji guda biyar a Labanon bayan wa’adin janyewa.
Jakadan Isra’ila mai barin gado zuwa Amurka, Michael Herzog, ya ce yana da tabbacin cewa Tel Aviv da Washington za su “kai ga fahimta” a kan lamarin, kuma za a ba su damar ƙarin lokaci.
