Sojojin Yaman Sun Gudanar Da Ayyuka 2 Akan "Yaffa"Da Kuma "Eilat"

 


A ci gaba da goyon bayan al'ummar Palastinu da na Labanon da kuma turjiya, sojojin Jirage Marasa Matuka (UAV) na Dakarun Yaman sun kai hari kan wani wuri na Sojojin makiya "Isra'ila" a yankin yaffa da suka mamaye da jirgi mara matuki mai suna "Jaffa", sannan kuma sun kai hari kan wani wurin sojojin mamaya a yankin Umm al-Rashrash [Eilat] ta hanyar amfani da jirage marasa matuka na Samad-4 guda hudu.


Ayyukan guda biyu sun cimma nasara, da taimakon Allah Ta’ala sun cimma manufofinsu.

 

Dakarun Yaman suna jinjinawa dukkanin mayaka masu tsayin daka a Palastinu da Lebanon domin kare al'ummar kasar a daidai lokacin da suke fuskantar hare-haren wuce gona da iri na Isra'ila da Amurka da kuma makircinsu na murkushe dukkan kasashe da al'ummomi.


Suna kara tabbatar da goyon bayansu na zahiri ga al'ummar Palastinu da na Labanon har sai an yi galaba a kan wuce gona da iri da kuma dakile shirinsu na aikata laifuka da kuma makirci.


Dakarun Yaman suna kira ga dukkanin kasashen Larabawa da na Musulmi da su kawar da shirun da suke yi, su zo su kuma taka rawar gani a wannan yakin, duk da cewa an kusa cika shekarar farko na farashi, kuma za mu ci gaba, da taimakon Allah har sai an cimma nasarar da aka yi alkawari.

Post a Comment

Previous Post Next Post