An Samu Munanan Fashe-fashe A Sansanonin Soji Na Gwamnatin Sahyoniyawa Bayan Harin Makami Mai Linzami Da Iran Ta Kai

 


Kafofin yada labaran gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila sun bayar da rahoton cewa, an samu tashin bama-bamai masu yawa a wasu sansanonin soji na gwamnatin, sakamakon harin makami mai linzami na Iran.


A cewar kamfanin dillancin labaran Falasdinu 'Sama', Kakakin rundunar yahudawan sahyoniya ya sanar da cewa, makamai masu linzami na Iran kai tsaye sun afkawa tsakiya da kudancin yankunan da aka mamaye.


A cewar wannan rahoto, sansanonin soji na gwamnatin sahyoniyawan sun fuskanci fashe-fashe a jere da munanan hare-hare sakamakon tasirin makamai masu linzami na Iran.

Post a Comment

Previous Post Next Post