Sheikh Naim Qassem, mataimakin shugaban kungiyar Hezbollah, ya bayyana cewa Harin Ambaliyar Al-Aqsa da Hamas ta kaddamar a ranar 7 ga Oktoba 2023 na nufin farkon sauya yanayin Yammacin Asiya tare da hadin gwiwar rundunar gwagwarmaya.
Sheikh Qassem ya jaddada cewa wannan aiki yana da matukar muhimmanci wajen canza al’amuran yankin da ke fama da tashin hankali. Ya ce, "Harin Ambaliyar Al-Aqsa yana da matukar tasiri, kuma yana nufin farawa na sauyi a yankin Yammacin Asiya tare da halartar rundunar gwagwarmaya."
A cewarsa, manufofin gwamnatin Isra’ila sun haɗa da ƙoƙarin kawo ƙarshen 'Yan Gwagwarmaya da kuma kisan gilla ga al’ummar Falasdinawa, yana mai cewa al’ummar Falasdinawa ba za su yarda da wahalhalun da suke fuskanta daga Isra’ila ba, suna da niyyar ci gaba da gwagwarmayar su don kare hakkin su.
Ya jaddada cewa Amurka da wasu ƙasashen Turai na da hannu a cikin dukkan laifukan da ake aikatawa a Gaza.
Har ila yau, ya jaddada haɗin kai a cikin Lebanon, yana goyon bayan shugaban majalisar dokokin Lebanon, Nabih Berri, a cikin ƙoƙarinsa na kaiwa ga tsagaita wuta. Sheikh Qassem ya bayyana cewa Hezbollah ba za ta yi watsi da burinta na yaki da Isra’ila ba, kuma suna shirin bayyana sabon shugaban kungiyar bayan zaben wanda zai maye gurbin Nasrallah.
Sheikh Qassem ya yi imanin cewa tarihi ya nuna cewa gwamnatin Isra’ila barazana ce ga yankin da duniya baki daya.
