Kungiyar Hamas ta zargi Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu da kawo cikas ga yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza, biyo bayan gazawar tattaunawar da aka yi a Doha.
Hamas ta yi ikirarin cewa dabarun Netanyahu na jinkirtawa da kuma kawo sabbin sharuddan da suka hada da kin amincewa da tsagaita bude wuta na dindindin da kuma janyewa daga Gaza, sun kawo cikas ga tattaunawar.
Duk da wannan, an shirya wani sabon zagaye na tattaunawa a mako mai zuwa, yayin da shugaban Amurka Joe Biden ya bayyana kyakkyawan fata game da yuwuwar yarjejeniyar.
Hamas dai na ci gaba da jajircewa kan yarjejeniyar da ta cimma a baya tare da yin kira ga masu shiga tsakani da su matsa wa Isra'ila lamba kan aiwatar da ita, yayin da al'amura ke ci gaba da tabarbarewa a Gaza tare da ci gaba da cin zarafi kan fararen hula Falasdinawa.
