Shugaban hukumar kula da harkokin kasashen waje ta (SCFR) Kamal Kharrazi ya ce alakanta harin roka na baya-bayan nan a Tuddan Golan da kungiyar Hizbullah wani sabon makirci ne na gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila.
A cikin wata hira da IRNA ta buga a ranar Talata, Kharrazi ya mayar da martani ga da'awar gwamnatin sahyoniyawan a kan kungiyar Hizbullah.
A yammacin Lahadin da ta gabata akalla mutane 12 ne suka mutu sannan wasu 30 suka jikkata sakamakon wani harin roka da aka kai a filin wasan kwallon kafa da ke garin Majdal Shams a yankin Golan na kasar Siriya da Isra'ila ta mamaye.
Kharrazi ya ce gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila na neman yaɗa yaƙin da take yi ne da yin ikirarin cewa kungiyar Hezbullah ta kaddamar da hari a Golan.
Ya kira da'awar gwamnatin sahyoniyawan a matsayin abin dariya ganin yadda mazauna Golan ke adawa da gwamnatin Isra'ila tare da fitowa kan tituna don gudanar da zanga-zangar kin jinin Netanyahu a jiya.
Ta yaya Hezbollah ta Labanon - mai kawance da Siriya - za ta kai harin bam a Golan na Siriya? shugaban SCFR ya tambaya.
Kharrazi ya shawarci gwamnatin kasar da ta kawo karshen mummunan yakin da ake ci gaba da yi a zirin Gaza.
Ya ci gaba da cewa, idan har aka ci gaba da yaki a yankin, ba abin da zai kawo illa kashe-kashe da barna.
