Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen, Sayed Abdulmalik Badruldeen Al-Houthi, ya yi watsi da shirin Amurka na tsagaita bude wuta a Gaza, yana mai bayyana cewa babu wasu Tabbatattun sharudda.
A jawabin da ya yi a ranar 6 ga watan Yuni, Al-Houthi ya jaddada cewa, matakin na Amurka yana taimakawa ne kawai a siyasance wajen goyon bayan yahudawan sahyoniya, kuma ba zai kai ga dakatar da wuce gona da irin da suke yi ba, ko janyewar makiya, ko isar da kayayyakin jin kai zuwa Gaza ba. Har ila yau, ya bayyana yadda Amurka ta shiga cikin laifukan da yahudawan sahyoniya suke aikatawa kan al'ummar Palastinu da kuma yadda Washington ke murkushe yunkurin dalibai da ayyukan tallafawa Falasdinu.
Al-Houthi ya yi nuni da cewa, gwamnatin sahyoniya ta ci gaba da yakin kisan kare dangi da take yi wa al'ummar Falastinu a Gaza a rana ta 244 a jere, tare da gina matsugunan da za su ci gaba da kai hare-hare kan birnin Quds. Ya kara da cewa mayakan gwagwarmayar Musulunci na ci gaba da tsayawa tsayin daka da kuma tunkarar makiya yahudawan sahyoniya, inda suke gudanar da dabarun yaki da hare-hare a yankunan da Isra'ila ta mamaye da kuma hanyoyin ruwa daban-daban.
Wannan bayani na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin Gaza ya shiga wata na takwas, inda aka samu rahotannin asarar rayukan fararen hula da kuma lalata kayayyakin more rayuwa da dama.
