Jami'an tsaron kasar Yemen sun yi nasarar kama Wasu 'Yan leken asiri da ke aiki da hukumomin leken asirin Amurka da Isra'ila. 'Yan leken asirin sun kutsa kai cikin manyan cibiyoyin tattalin arziki da suka hada da bankuna da ma'aikatu don tattara bayanai da kuma yin zagon kasa.
Furucin 'yan leken asirin ya nuna cewa an dora musu alhakin tattara muhimman bayanai kan harkokin man fetur da gas da ma'adinai na Yemen. Amurka ta yi niyyar amfani da wannan bayanan don samun tasirin tattalin arziki a Yemen.
Hakan na zuwa ne bayan da kasar Yemen ta sanar da kame wata cibiyar leken asiri mai alaka da CIA da ke aiki a kasar. Gwamnatin Yemen ta lashi takobin daukar mataki kan tsoma bakin kasashen waje da kuma leken asiri.
Wannan ci gaban ya nuna yadda ake ci gaba da zaman dar-dar a tsakanin kasar Yemen da Amurka da Isra'ila, kuma yana nuna muhimmancin 'yancin kai da tsaron kasar Yemen.
