Kungiyar Hizbullah Takai Hare Haren Makamai Masu Linzami Akan HKI

 


Kafofin yada labaran kasar Lebanon sun bayyana cewa, kungiyar Hizbullah ta harba makamai masu linzami da rokoki da dama a wuraren da HKI ta Mamaye a Arewacin Falasdinu.


Tashar talabijin ta Al Mayadeen ta fada a ranar Laraba cewa an ji karar sautin amsa kuwwa mai Alamta zuwan Makamai bayan hare-haren da aka kai a arewacin Falasdinu data mamaye.


Kafafen yada labaran yahudawan sahyoniya sun kuma bayyana cewa, kusan makamai masu linzami 30 ne kungiyar Hizbullah ta harba wadanda suka lalata gine-gine tare da haddasa gobara a sassa daban-daban na Qiryat Shemona.


Kungiyar Hizbullah a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce takai hari a kan wani barikin HKI a yayin harin.


Tun bayan kaddamar da farmakin yahudawan sahyuniya akan zirin Gaza ne dakarun Hizbullah suka fara kai hare-hare kan sansanonin yahudawan sahyuniya domin rage matsin lambar da HKI ke yi wa al'ummar Gaza.

Post a Comment

Previous Post Next Post