Jami'ar Kasa ta Asturaliya na Kora tare da Hukunta Dalibai Saboda Goyon Bayan Falasdinu

 


Jami'ar kasar Australia (ANU) ta kori dalibai biyu tare da hukunta wasu 10 saboda zanga-zangar goyon bayan Falasdinu da kuma kalamai a harabar jami'ar.


A cewar rahoton daren Juma'a na IRNA daga kamfanin dillancin labaran Anadolu, An kori Beatrice Tucker, dalibar dake karatu a bangaren visual arts, tare da dakatar da ita daga jami'ar, bayan ta yi tsokaci a wani shirin rediyo na goyon bayan gwagwarmayar Falasdinu da kuma kin yin Allah wadai da Hamas. 


Wannan dalibi ta ce a cikin wannan shirin na rediyo, "Hamas ta cancanci goyon bayanmu ba tare da wani sharadi ba."


Wata kungiyar da ke goyon bayan Falasdinu a jami'ar ta ce a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce Tucker ta fuskanci koma baya daga kafafen yada labarai da kungiyoyin yahudawan sahyoniya, lamarin da ya kai ga korar ta.


 Finian Colwell dan kungiyar ya soki matakin da jami'ar ta dauka tare da yin kira da ta yanke alaka da Isra'ila.

Post a Comment

Previous Post Next Post