Ministan tsaron Pakistan ya yi Allah wadai da harin da Isra'ila ta kai kan karamin ofishin jakadancin Iran da ke Damascus a matsayin cin zarafi. Martanin tsaron da Tehran ta yi ya yi daidai da harin.
Khawaja Muhammad Asif a ranar Litinin din nan ya yi Allah wadai da harin da Isra'ila ta kai kan harabar diflomasiyyar Iran da ke Damascus wanda ya kai ga kisan wasu manyan mashawartan soji 7 ciki har da wani babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran (IRGC).
A yayin wani baje kolin, ya bayyana cewa, Isra'ila ta yi fito-na-fito da keta dokokin kasa da kasa, ta hanyar kai hari kan karamin ofishin jakadancin Iran, kuma Iran na da hakkin mayar da martani.
Asif ya kara da cewa haramtacciyar Kasar ce ta kai hari kan tawagar Iran a Damascus saboda tsananin goyon bayan da Tehran ke baiwa Falasdinu.
Ministan tsaron kasar ya kuma jaddada goyon bayan kasarsa ga al'ummar Gaza, yana mai cewa Islamabad na matukar goyon bayan Falasdinawa.
Ya bayyana damuwarsa kan yadda tashe-tashen hankula a yammacin Asiya zai iya yin tasiri ga sauran kasashe kamar Pakistan. Ya kuma yi gargadin cewa kasashen da ke goyon bayan Isra'ila suma za su iya shiga cikin wutar yaki.
"Ba ma son tashin hankali ya karu, duk da haka, dole ne a dakatar da kisan gillar da ake yi wa Falasdinawa," in ji Asif, mai shekaru 74, yayin da yake magana a shirin Geo News' Capital Talk.
Ya jaddada cewa sadaukarwar da Falasdinawan suke yi ba zai zama a banza ba, yana mai bayyana fatansu na samun 'yancin kai nan gaba kadan.
Bugu da kari, ya bayyana cewa Pakistan ba ta cikin kowane irin matsin lamba na amincewa da Isra'ila.
