Amurka ta kakabawa Iran sabbin takunkumai saboda harin da ta kai kan Isra'ila

 


Amurka ta ƙara takunkumi kan sashen man fetur da sinadaran petrochemicals na Iran, saboda harin ramuwar gayya da Iran ta kai kan wuraren Isra'ila. 


Ma'aikatar Baitulmalin Amurka ta bayyana cewa sun kulle kadarorin kamfanoni 10 da jiragen ruwa 17 da suka taimaka wajen jigilar man fetur da kayan sinadarai na Iran. Takunkumin na nufin takura wa Iran a bangaren kudaden shiga, musamman wadanda take amfani da su don tallafawa gwagwarmayar ƙungiyoyin gwagwarmaya a yankin Gabas ta Tsakiya.


Amurka ta ce wannan takunkumi yana nufin hana Iran samun kudaden shiga daga man fetur, wanda take amfani da shi wajen samar da makamai da kaddamar da shirye-shiryenta na soja. Iran ta ce wannan tsare-tsare nata na soja na kariya ne, kuma ta zargi Amurka da amfani da takunkumi don haifar da matsalolin tattalin arziki ga al'ummarta.


Sakataren Baitulmalin Amurka Janet L. Yellen ta ce takunkumin Amurka yana nufin hana Iran damar ci gaba da daukar matakan da suke tayar da hankali a yankin, ciki har da ci gaba da shirye-shiryenta na makamai da na nukiliya.


Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken ya kara da cewa Amurka za ta ci gaba da kakaba wa Iran takunkumi muddin tana amfani da kudaden shigar man fetur wajen kai hare-hare da tallafa wa ayyukan ta'addanci a duniya.


Wannan takunkumin ya zo ne karkashin doka mai suna "Stop Harboring Iranian Petroleum Act" da ke hukunta duk wani wanda ya shiga cikin cinikayyar man fetur na Iran.


A ranar 1 ga Oktoba, Iran ta kai hari da jerin makamai kan sansanonin soji da na leƙen asirin Isra'ila, a matsayin ramuwar gayya kan kisan shugaban Hamas, Hezbollah, da IRGC da Isra'ila ta yi. Iran ta ce wannan hari da ta kai ya samu nasara fiye da kashi 90 cikin 100, kuma bai saɓa da dokokin kasa da kasa ba.

Post a Comment

Previous Post Next Post